Hausa
Surah Al-Layl ( The Night ) - Aya count 21
وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ
( 1 ) 
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
وَالنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ
( 2 ) 
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
وَمَا خَلَقَ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ
( 3 ) 
Da abin da ya halitta namiji da mace.
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ
( 4 ) 
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَاتَّقَىٰ
( 5 ) 
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
وَصَدَّقَ بِالْحُسْنَىٰ
( 6 ) 
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْيُسْرَىٰ
( 7 ) 
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
وَأَمَّا مَن بَخِلَ وَاسْتَغْنَىٰ
( 8 ) 
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
وَكَذَّبَ بِالْحُسْنَىٰ
( 9 ) 
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْعُسْرَىٰ
( 10 ) 
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
وَمَا يُغْنِي عَنْهُ مَالُهُ إِذَا تَرَدَّىٰ
( 11 ) 
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ
( 12 ) 
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
وَإِنَّ لَنَا لَلْآخِرَةَ وَالْأُولَىٰ
( 13 ) 
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّىٰ
( 14 ) 
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
لَا يَصْلَاهَا إِلَّا الْأَشْقَى
( 15 ) 
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
الَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
( 16 ) 
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
وَسَيُجَنَّبُهَا الْأَتْقَى
( 17 ) 
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
الَّذِي يُؤْتِي مَالَهُ يَتَزَكَّىٰ
( 18 ) 
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَىٰ
( 19 ) 
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
إِلَّا ابْتِغَاءَ وَجْهِ رَبِّهِ الْأَعْلَىٰ
( 20 ) 
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ
( 21 ) 
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).